September 18, 2026

Majigiri Ya Sake Ɗarewa Kan Kujerarsa Ta Shugabancin Jam’iyyar PDP A Jihar Katsina.

0

A karo na biyu, Hon. Salisu Yusuf Majigiri ya sake komawa matsayinsa na shugabacin babbar jam’iyyar adawa ta PDP a jihar Katsina.

In dai ba a manta ba, Majigiri ya ajiye shugabancin jam’iyyar ta PDP ne bisa raɗin kansa gab da lokacin kakar gudanar da za6ukan fidda gwanin jam’iyyu a watannin baya, inda ya yanke shawarar shiga neman tikitin takarar kujerar gwamnan jihar Katsina a jam’iyyarsa ta PDP.

Sai dai biyo bayan za6en fidda gwanin na jam’iyyar PDP da ya gudana wanda Allah bai ba shi sa’a a kanta ba, sai yanzu kuma aka sake ba shi jagorancin jam’iyyar ta PDP a matakin jiha.

Tuni dai Hon. Majigiri ya ci gaba da jagorantar sasanta ‘ya’yan jam’iyyar da kuma ɗinke duk wata ɓaraka domin samun nasararsu a zaɓukan 2023 da ake fuskanta.

Babban abin da ke a gaban jam’iyyar ta PDP dai a yanzu shi ne, fitar da wanda zai yi wa Sanata Yakubu Lado Ɗanmarke mataimaki wanda shi ne aka tsaida a matsayin ɗan takarar gwamnan jihar a 2023.

About The Author

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *