2023: Ni Kaɗai Ne Ɗan takarar Shugabancin Ƙasa A APC — Tinubu
Jagoran jam’iyyar APC na ƙasa kuma ɗan takarar shugaban kasa a jam’iyyar, Bola Ahmed Tinubu, ya ce shi kaɗai ne ɗan takarar shugaban kasa a zaben 2023.
Ya bayyana hakan ne a yau Juma’a yayin da yake jawabi ga wakilan jam’iyyar APC a gidan gwamnatin Jihar Neja, Minna gabanin zaben fidda-gwani da za a yi.
Tinubu ya bayyana cewa ci gaban da ya samu a matsayinsa na tsohon gwamnan jihar Legas, tarihi ne cewa shi kadai ne zai iya ceto kasar nan daga halin da ta ke ciki.
“Ni kadai ne ke takarar shugabancin kasarmu mai girma, ban san inda wasu masu gudu za su je ba; Ni kadai ne nasan hanyar ci gaban kasa.
“Ni dai na fi kowa zama wanda ya dace da takara saboda tarihi na, na ɗaga mutane da dama, tun daga kansiloli, ’yan majalisa, majalisar dattijai, wakilai da gwamnoni, amma duk da haka suna nuna min yatsa.
“Za mu hada hannu don sake gina Najeriya wacce mu ke buƙata, kada ku damu da su; Ni kadai ne a cikin tseren, ku biyo ni ba zan batar da ku ba, ni kadai ne ke da ilimi da kwakwalwar da zan yi wa Najeriya tunani.
“Ina da kwarin gwiwa, na yi hakan a Legas kuma zan zame wa Nijeriya alheri,” in ji shi.
