September 18, 2026

Kusoshin Gwamnati Da Manyan ‘Yan Kasuwa Na Cigaba Da Kawowa Mangal Ta’aziya

0

Daga Awwal Isah, Katsina

Manyan mutane daga sassa daban daban na Nigeria na ci gaba da zuwa nan jahar Katsina don yin ta’aziyya bisa rasuwar mahaifiyar Alhaji Dahiru Bara’u Mangal, Hajiya Murja.

Gwamnan jahar Katsina Aminu Bello Masari da mataimakin shi Mannir Yakubu na cikin mutanen dake gidan Dahiru Mangal don tarbar masu zuwa yin ta’aziyya.

Daga cikin mutanen da suka zo yin ta’aziyya akwai gwaman jahar Jigawa Badaru Abubakar, dana jahar Bauchi Sanata Bala Muhammad, da kuma gwamnan jahar Barno Babagaba Umara Zulum.

Sauran sun haɗa da shugaban majalissar dattawan Nigeria Ahmad Lawan, wanda ya jagoranci wasu ƴan majalissar dattawa zuwa yin taaziyya, da kuma kakakin majalissar dokokin jahar Katsina Tasi’u Musa Maigari, wanda shima ya jagoranci wasu ƴan majalissar dokokin jahar Katsina zuwa yin ta’aziyya.

About The Author

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *