September 17, 2026

Rundunar Yan Sandan Najeriya A Jihar Katsina Ta Dakile Hari.

0

Bayanin hakan na ƙunshe ne a cikin wata sanarwa da mai magana da yawun rundunar SP Isah Gambo ya fitar.

Sanarwar ta ce rundunar ta samu wannan nasarar ne bayan samun kiran gaggawa a ranar 14/09/2022 da misalin 14:45 cewa wasu yan ta’adda kimanin 30 saman babura ɗauke da bindigu kirar AK47 sun tare hanyar Sabuwa zuwa Mararabar Yakawada da ke cikin karamar hukumar Sabuwa ta jihar Katsina.

Ta ce bada ɓata lokaci ba baturen yan sandan karamar hukumar Sabuwa ya jagoranci tawaga zuwa yankin, tare da farma su da ruwan wuta.

Kamar yadda ta ce, cikin ikon Allah tawagar ta dakile harin, aka kashe dan ta’adda ɗaya, aka samu bindiga AK47 ɗaya, tare da ababen hawan yan ta’addan hudu.

About The Author

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *