Mun Hakura Da Kayan Aure, Amma Namiji Zai Baiwa Budurwa Naira 700,000 Cewar Kungiyar ‘Yan Mata Da Zawarawa Ta Mayo Belwa
Kungiyar ‘yan mata da zawarawa ta karamar hukumar Mayo Belwa a jihar Adamawa, ta gindaya sharudda ga mazan da ke son aure a karamar hukumar.
Shugabar kungiyar ta ce sun cimma abubuwa da dama a taron da suka yi inda ta ce “abu na farko da muka cimma shi ne mutane susan cewa ba gwanjon mata akeyi a Mayo Belwa ba”.
Ta ce ” Mun fitar da batutuwa game da da sadaki, za mu iya daga sadaki idan namiji zai biya sadaki da sauki to zai yi wa mace kayan aure, bayan haka kuma daga randa aka yi aure ta koma gidanshi kayan sun zama nata”.
Fatima ta ce “Abu na biyu baza akai mace da komai daki ba ko da kuwa kayan kicin ne saboda muma bama bukatar komai daga wajen mazajen”.
Shugabar kungiyar matan ta kara da cewa ” Idan kuma har ba za su iya yin kayan daki ba za su ba wa mata kudi idan bazawarace daga dubu 300 zuwa sama sannan idan budurwa ce daga dubu 700 zuwa sama, kayan aure mun hakura da shi domin dama wani abu ne da ke ba wa mata wahala”.
“Abu na gaba kuma shi ne idan har namiji yazo ya tambayi auren mace to a ayi bincike game da lafiyarsa da kuma asalinsa, wadannan sune abubuwan da muke bukata majalisar harkokin addinin musulunci ta Mayo Belwa ta sanya hannu kansu” inji Fatima.
Fatima Ahmad, a wajen taron na su har da jami’an majalisar harkokin addinin musuluncin sun zo, kuma sun ji abubuwan da aka tattauna a wajen.
Shugabar kungiyar ta ce, tasowar wannan batun ne ya sa suka kafa kungiyar ‘yan mata da zawarawan kuma sun samu goyon baya sosai daga wuajen ‘yan matan gari da zawarawan har ma da majalisar dake kula da harkokin addinin musuluncin kanta.
Samari shin ko kun amince da wannan sharadin?
