September 18, 2026

Hon. El-Marzuq Ya Musanta Zargin Da Ake yi Masa Game Da Kama Hon. Shehu Abdu Daura

0

Daga El-Zaharadeen Umar, Katsina

Kwamishinan Shari’a kuma Baban antoni na jihar Katsina Hon Ahmad Usman El-Marzuq ya musanta sa hannunsa game da cece kucen da ake yi na kama Hon. Shehu Abdu Daura

Haka Hon. El-Marzuq ya bada tabbacin bayyana gaban kafafen yada labarai domin kare kansa daga wancan batu da ake ce shi ne kanwa uwar gamin kama dan takara shugaban karamar hukumar Daura a karkashin jam’iyyar APC a zabe mai zuwa.

Duk lokacin da Hon. El-Marzuq ya tattauna da manema labarai zaku ji yadda zata kaya a wannan kafa ta Popular News Hausa.

Idan za a iya tunawa an kama Hon. Shehu Abdu Daura bisa wasu zarge-zarge da aka ce wasu sun rubuta zuwa ga ‘yan sanda inda har batun ya kai zuwa kotu.

About The Author

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *