Ayi Hattara Da Cin Zarafin Fulani A Najeriya
Daga Muazu Hardawa
Matsalar fulani makiyaya a Najeriya idan aka ci gaba da kashe su ana kwashe dukiyar su ana tsiyata su, lamarin ba zai yiwa kowane mutum da gwamnatoci dadi ba nan gaba.
Saboda idan har fulani suka tsiyace suka rasa wajen zama suka rasa kwanciyar hankali, kowa ya sani suna da yawa suna da dauriya da kasa jure wulakanci kuma suna nan a ko ina, basu iya noma ba basu iya kasuwanci.
Idan manyan su sun yi hakuri da talauci da wahala, matasan fulani ba za su iya hakuri ba illa su nemi rayuwa ko da tsiya ko da arziki ta hanyat ta’adda da aikata miyagun ayyuka don neman abin duniya da rayuwa ta kowane hali.
Idan haka ta kasance kasar kanta zata iya lalacewa fiye da duk wata matsala data auku a baya.
Gwamnatoci da masu arziki da sauran jamaa ayi hattara a fiskanci gaskiya a daina sayar da dazuka ana korar fulani daga mazaunansu saboda kasa tayi dadi tayi daraja.
Idan ba haka ba, za a zo lokacin da kowa zai tara dukiya su hana shi kwanciyar hankalin da zai zauna ya ci a inuwa.
Da fata Allah ya kawo mafita kan wannan matsala ta uzurawa fulani a Najeriya
