Daga El-Zaharadeen Umar, Katsina
Jam’iyyar APC mai mulkin jihar Katsina ta bayyana dalilinta na sauya dan takarar shugaban karamar hukumar Daura wanda ya ci zaban fidda gwani Hon. Shehu Abdu Daura inda ta maye gurbinsa da wanda ya zo na biyu Bala Musa
Da yake bayyana dalilan ga manema labarai a Katsina mataimakin shugaban jam’iyyar APC na jihar Katsina Bala Abubakar Musawa ya kara da cewa yin haka shi ne kaɗai mafita a wannan yanayi da ake ciki.
“Yau juma’a hukumar zabe mai zaman kanta ta jihar Katsina, ke rufe karbar sunayen ‘yan takara, mu kuma namu wanda ya ci zaban fidda gwani yana fama da matsalolin shari’a, haka tasa dole muka canza sunansa da wanda ya zo na biyu domin gudun kadda mu rasa baki daya” inji Bala Abu.
Bala Abu ya kara da cewa hakika Shehu Abdu shi ne ya lashe zaben fidda gwani da aka gudanar a ranar 9 ga watan Fabrairu,2022 to amma zarge zargen da suka dabaibaye shi kamar zargin zamba cikin aminci da cutarwa da kuma mallakar kudin da ba nasa ba, tasa dole aka jingine batunsa sai kotu ta yi aikinta.
Ya ce kamar yadda dokar ƙasa ta yi bayani a sashe na 66 (1), 107,(1),137 (1) da kuma 182 (1) cewa duk wani mutum da ke neman kowace irin kujera harda ta shugaban ƙaramar hukuma dole ya kasance baya fuskantar rashin gaskiya da zamba cikin aminci da saura laifuffuka.
A cewarsa haka abin yake a dokar ƙananan hukumomi ta jihar Katsina ta (2000) wanda ta ce ana iya amincewa da dan takara ko kin amincewa da shi idan yana fuskantar irin wancan matssla musamman mutumin da ke neman shugabancin ƙaramar hukuma.
“Sashe na 107(1) na dokar kananan hukumomi ta (2010) sashi na 7(2) da jihar Katsina ta zabe ta (2002) da sashi 29 (1) ta dokar jihar Katsina ta (2000) duk sun yi bayani ƙarara akan wanann batu’ inji shi.
Ya ce wannan mataki ba na dindindin bane da zaran kotu ta gama aikinta kafin ranar zabe wanda ya ci zaban fidda gwani Shehu Abdu zai koma kan matsayinsa idan kotu ta wanke shi, idan kuma an samu aƙasin haka daman an bada wanda zai canje shi.
A cewar Bala Abubakar Musawa wannan ita ce matsayar jam’iyyar APC ta jihar Katsina ba wai matsayar wani mutum guda ba kowa wasu mutane ba.
